:
Breaking News

Sojojin Operation HADIN KAI Sun Cafke Mutane Biyar da Ake Zargi da Garkuwa da Mutane a Yobe

https://ngazargamuexpressnews.com.ng/public/frontend/img/header-adds/adds.jpg

Rundunar Sojojin Operation HADIN KAI, ta Sashi na 2, tare da haɗin gwiwar Kungiyar Maharba ta Jihar Yobe, sun yi nasarar cafke wasu mutane biyar da ake zargi da aikata laifin garkuwa da mutane a ƙauyen Jegalari da ke Ƙaramar Hukumar Fune ta Jihar Yobe.

An gudanar da samamen ne a ranar 23 ga Yulin 2026 bayan samun sahihan bayanan sirri kan ayyukan waɗanda ake zargin. Sojojin Bataliya ta 233 da ke Sansanin Sojoji na Damaturu ne suka jagoranci wannan aiki.

A yayin samamen, jami'an tsaro sun ƙwato bindigogi uku ƙirar AK-47 da aka ƙera a gida, bindiga guda ɗaya da aka ƙera a gida, harsasai iri-iri da kuma wayoyin hannu guda huɗu da ake zargin ana amfani da su wajen gudanar da ayyukan ta'addanci.

A halin yanzu, mutanen da aka kama suna tsare a hannun sojoji domin ci gaba da bincike, tare da gano irin rawar da suka taka a harkokin garkuwa da mutane da sauran laifuffuka.

Rundunar Operation HADIN KAI ta sake jaddada aniyarta ta ci gaba da gudanar da hare-haren da suka dogara da bayanan sirri domin murƙushe 'yan ta'adda da sauran masu aikata laifuffuka a yankin Arewa maso Gabas.

Har ila yau, rundunar ta yi kira ga al'umma da su kasance masu sanya ido tare da kai rahoton duk wani mutum ko motsi da ake zargi ga hukumomin tsaro mafi kusa, tana mai bayyana cewa sahihan bayanan jama'a na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al'umma.

https://ngazargamuexpressnews.com.ng/public/frontend/img/header-adds/adds.jpg

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *